LabaraiWasanni

Ƙasar Benin ta shige gaban Najeriya a rukunin sharar fagen shiga gasar cin kofin duniya na ƙwallon ƙafa.

Ƙasar Benin ta samu damar hawa kan jadawalin rukunin da ya kunshi Najeriya da Rwanda da Zimbabwe da Afrika ta Kudu da kuma Lesotho a gasar sharar fagen neman kaiwa ga shiga gasar cin kofin duniya na ƙwallon ƙafa.

Benin wacce tayi wasan ta a ranar Alhamis da kasar Zimbabwe ta hada maki 8 daga wasanni 5, biyo bayan tashi daga wasa tsakanin ta da Zimbabwe kowacce ƙasa na da ci biyu.

A gobe juma’a ne dai za’a fafata tsakanin Rwanda, wacce ke a matsayi na biyu a rukunin da maki 7 da kuma Najeriya wacce ke s matsayi na biyar da maki 3 a Kigali babban birnin Rwanda yayin da Afrika ta Kudu wacce ke da maki 7 za ta kara da ƙasar Lesotho.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button