
Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Afrika CAF, ta ayyana sunan alkalin wasan da zai jagoranci wasan da ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta ƙasa Super Eagles za tayi da Deserts Foxes na Algeriya.
A cewar rohotannni, Omar Artan, Alkalin wasa daga ƙasar Somalia,shine zai jagoranci alkalanci wasan Najeriya da Algeriya.
Rohotannni sun bayyana Omar Artan, a matsayin fitattacen alkalin wasa, kuma ya jagoranci da dama daga cikin wasannin a ciki da wajen nahiyar Afrika.
Najeriya dai za ta fafata wasan matakin dab dana kusa dana ƙarshe watau Quarter Finals da ƙasar Algeriya a ranar Asabar mai zuwa da misalin karfe biyar na yamma.









