LabaraiLafiya

WHO ta buƙaci Isra’ila ta saki ma’aikacinta da aka kama a Gaza

Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ya bukaci Isra’ila ta saki wani ma’aikacin hukumar da ya ce sojojin Isra’ila sun kama a wani farmaki da suka kai a tsakiyar Gaza ranar Litinin.

Tedros Ghebreyesus ya ce sojojin sun jefa ma’aikatan agaji da iyalansu cikin hatsari a lokacin da suka shiga gidajensu da kuma babban dakin ajiyar kaya a Deir al-Balah.

Ya yi alƘawarin cewa WHO za ta ci gaba da gudanar da ayyukanta a yankin.

Deir al-Balah dai na cike makil da Falasɗinawa da suka rasa matsugunansu a kusan shekaru biyu na yakin Gaza

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button