
Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta bayar da belin Sanata Natasha kan kuɗi naira miliyan 50.
Haka kuma kotun ta ɗage ƙarar zuwa ranar 23 ga watan Satumba domin ci gaba da sauraronta.
Gwamnatin Najeriya ce dai ta gurfanar da ƴarmajalisar a gaban kotu kan zargin ɓata sunan Shugaban Majalisar Dattawa, Godswil Akpabio da tsohon gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello.









