LafiyaSiyasa

Ya kamata Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu ya san cewa shi shugaban Najeriya ne, ba Gwamnan jihar Legas ba – A cewar Peter Obi.

Dan takarar jam’iyyar Labour Party a zaɓen da ya gabata, Peter Obi, yayi kira ga Shugaban Kasa, Bola Ahmad Tinubu kan ya dinga nuna kishi kasa a al’amurran sa na rayuwa, ganin cewar a yanzu fa Najeriya ya ke shugaban ta ba wai jihar Legas ba.

A cewar Peter Obi, kamata yayi Shugaba Bola Ahmad Tinubu ya kasance yana gabatar da bukukuwa sa a sassa daban-daban na Najeriya a matsayin sa na shugaba, ba wai a jihar Legas kaɗai ba.

“Kamata yayi mu ga shugaban Najeriya ya halarci bikin Sallah a Sokoto ko kuma bikin Kirsimeti a Anambra, wannan shine zai kara kyautata hadin kai da cigaban ƙasa, inji Peter Obi”.

Da ya juya kan gyaran dokar zaɓe, dan takarar na jam’iyyar LP, Peter Obi, ya bayyana aikin a matsayin babban kalubale da zai kai ga samun zaɓen da al’ummar kasa zasu aminci dashi.

Daga karshe, Peter Obi, ya sharwarci shugabannin a matakai daban-daban dasu kyautata alaƙar su da wadanda suke wa jagoranci, yana mai cewa yin hakan zai taimaka wajen ganin an samu fahimtar juna tsakanin mai mulki da wadanda ake mulka.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button