KimiyyaLabarai

Za’a samu ruwan sama na tsawon kwanaki uku a wasu jihohi Najeriya.

Hukumar dake kula da yanayi ta Kasa NiMet, tayi harsashin cewa akwai yiyuwar samu ruwan sama kamar da bakin ƙwarya na tsawon kwanaki uku, a wasu daga cikin jihohi kasar nan.

A cewar NiMet, akwai yiyuwar jihohi kamar Cross River da Aka Ibom da Edo da Bayelsa da Delta da kuma Ogun su fuskanci samu ruwan sama daga ranar Laraba 9 ga watan Afrilu zuwa ranar Juma’a 11 ga wata.

Hakazalika, hukumar ta NiMet, tayi harsashin samun matsakaicin ruwan sama a jihohin Legas da Ondo da Delta da Imo da Abia da kuma Ekiti.

Hukumar tayi kuma gargadi cewar akwai yiyuwar samun iska mai karfi gaske, a don haka ta shawarci matafiya dasu kasance cikin shirin tare da kiyaye sharudan tuƙi a yayin ruwan sama.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button